Littafi Mai Tsarki

Luk 1:14-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Za ka yi murna da farin ciki,Mutane da yawa kuma za su yi farin ciki da haihuwa tasa.

15. Domin zai zama mai girma a wurin Ubangiji,Ba kuwa zai sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba.Za a cika shi da Ruhu Mai TsarkiTun yana cikin uwa tasa.

16. Zai kuma juyo da Isra'ilawa da yawa ga Ubangiji Allahnsu.

17. Zai riga shi gaba cikin ruhu da iko irin na Iliya.Yă mai da hankalin iyaye a kan 'ya'yansu,Yă kuma juyo da marasa biyayya su bi hikimar adalai,Ya tanada wa Ubangiji jama'a, ya same su a shirye.”

18. Sai Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta ƙaƙa zan san haka? Ga ni tsoho, maiɗakina kuma ta kwana biyu.”

19. Sai mala'ikan ya amsa ya ce, “Ni ne Jibra'ilu da yake tsaye a gaban Allah. An aiko ni ne in yi maka magana, in kuma yi maka wannan albishir.

20. To, ga shi, za ka bebance, ba za ka iya magana ba, sai a ran da al'amuran nan suka auku, don ba ka gaskata maganata ba, za a kuwa cika ta a lokacinta.”

21. Jama'a suna ta jiran Zakariya, suna mamakin jinkirinsa a Haikali.

22. Da ya fito, ya kāsa yi musu magana. Sai suka gane lalle an yi masa wahayi ne a Haikalin. Sai ya riƙa yi musu nuni, amma ba ya magana.

23. Sa'ad da kuma kwanakin hidimarsa suka cika, ya koma gida.

24. Bayan kwanakin nan mata tasa Alisabatu ta yi ciki. Sai ta riƙa ɓuya har wata biyar, tana cewa,

25. “Haka Ubangiji ya yi mini a kwanakin da ya dube ni da rahama, domin yă kawar mini da wulakanci a wurin mutane.”

26. A wata na shida Allah ya aiko mala'ika Jibra'ilu zuwa wani gari a ƙasar Galili, wai shi Nazarat,

27. gun wata budurwa da aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu, na zuriyar Dawuda, sunan budurwar kuwa Maryamu.