Littafi Mai Tsarki

Luk 20:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Wata rana yana koyar da mutane a Haikali, yana yi musu bishara, sai ga manyan firistoci da malaman Attaura, da shugabanni suka matso,

2. suka ce masa, “Gaya mana da wane izini kake yin abubuwan nan, ko kuwa wa ya ba ka izinin?”

3. Sai ya amsa musu ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku gaya mini,

4. baftismar da Yahaya ya yi, daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce?”

5. Sai suka yi muhawwara da juna suka ce, “In mun ce, ‘Daga Sama take,’ sai ya ce, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’

6. In kuwa muka ce, ‘Ta mutum ce,’ sai duk jama'a su jajjefe mu, don sun tabbata Yahaya annabi ne.”

7. Sai suka amsa masa, suka ce, ba su san daga inda take ba.

8. Yesu ya ce musu, “Haka ni kuma ba zan faɗa muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan ba.”