Littafi Mai Tsarki

Fit 24:13-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Sai Musa ya tashi, shi da baransa Joshuwa, suka tafi, suka hau dutsen Allah.

14. Ya ce wa dattawan, “Ku dakata a nan har mu komo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai ya je wurinsu.” Sa'an nan Musa ya hau bisa dutsen.

15. Da hawan Musa bisa dutsen, girgije ya rufe kan dutsen.

16. Ɗaukakar Ubangiji kuma ta zauna bisa Dutsen Sina'i. Girgijen ya lulluɓe dutsen har kwana shida, a rana ta bakwai kuwa Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.

17. Isra'ilawa suka ga ɗaukakar Ubangiji kamar wuta mai cinyewa a bisa ƙwanƙolin dutsen.

18. Sai Musa ya shiga girgijen, ya hau bisa dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba'in da dare arba'in.