Littafi Mai Tsarki

Fit 18:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. A sa'ad da suke da wata matsala sukan zo wurina, ni kuwa nakan daidaita tsakanin mutum da maƙwabcinsa, nakan kuma koya musu dokokin Allah da umarnansa.”

17. Amma surukin Musa ya ce, “Abin nan da kake yi ba daidai ba ne.

18. Kai da jama'an nan da suke tare da kai za ku rafke, saboda abin da kake yi ya fi ƙarfinka, kai kaɗai ba za ka iya ba.

19. Yanzu sai ka saurari maganata, zan ba ka shawara, Allah kuwa ya kasance tare da kai. Za ka wakilci jama'a a gaban Allah, ka kai matsalolinsu gare shi.

20. Ka koya musu dokokin da umarnan, ka nuna musu hanyar da ya kamata su yi.