Littafi Mai Tsarki

Fit 15:19-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Gama sa'ad da dawakan Fir'auna, da karusansa, da mahayan dawakansa suka shiga bahar, Ubangiji ya komar da ruwan bahar a bisansu, amma Isra'ilawa suka yi tafiya a busassiyar ƙasa ta tsakiyar bahar.

20. Sai Maryamu, annabiya, 'yar'uwar Haruna, ta ɗauki kuru cikin hannunta. Mata duka suka fita, suka bi ta da kuwaru suna ta rawa.

21. Maryamu tana raira musu waƙa tana cewa,“Raira waƙa ga Ubangiji, gama ya ci gawurtacciyar nasara,Doki da mahayinsa, ya jefar cikin bahar.”

22. Musa kuwa ya bi da Isra'ilawa daga Bahar Maliya, suka shiga jejin Sur. Suka yi tafiya kwana uku cikin jejin, ba su sami ruwa ba.

23. Sa'ad da suka zo Mara, sun kasa shan ruwan Mara saboda ɗacinsa, don haka aka sa masa suna Mara.

24. Sai mutanen suka yi wa Musa gunaguni suna cewa, “Me za mu sha?”