Littafi Mai Tsarki

Zab 69:10-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Na ƙasƙantar da kaina ta wurin yin azumi,Jama'a kuwa suka ci mutuncina.

11. Na sa tufafin makoki,Sai suka maishe ni abin dariya.

12. A tituna suna ta magana a kaina,Bugaggu da giya kuwa suna raira waƙa a kaina.

13. Amma ni, zan yi addu'a gare ka, ya Ubangiji,Ka amsa mini, ya Allah, a lokacin da ka zaɓa,Sabili da muhimmiyar ƙaunarka,Saboda kana cika alkawarinka na yin ceto.

14. Ka cece ni daga nutsewa cikin wannan laka,Ka kiyaye ni daga maƙiyana,Daga kuma wannan ruwa mai zurfi.

15. Kada ka bar ambaliyar ruwa ta rufe ni.Kada ka bar ni in mutu cikin zurfafa,Ko in nutse a cikin kabari.