Littafi Mai Tsarki

Zab 37:23-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Ubangiji yakan bi da mutum lafiyaA hanyar da ya kamata yă bi,Yakan ji daɗin halinsa,

24. In ya fāɗi, ba zai yi warwar ba,Gama Ubangiji zai taimake shiYă tashi tsaye.

25. Yanzu dai na tsufa, ni ba yaro ba ne,Amma ban taɓa ganin Ubangiji ya yar da mutumin kirki ba,Ko kuma a ga 'ya'yansa suna barar abinci.

26. A koyaushe yakan bayar a sake,Yana ba da rance ga waɗansu,'Ya'yansa kuwa dalilin albarka ne.

27. Ka rabu da mugunta ka aikata nagarta,Za ka kuwa zauna a ƙasar har abada,

28. Gama Ubangiji yana ƙaunar abin da yake daidai,Ba ya rabuwa da amintattun jama'arsa,Yana kiyaye su koyaushe,Amma za a kori zuriyar mugaye.

29. Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Su gāje ta har abada.

30. Kalmomin mutumin kirki suna da hikima,Yana faɗar abin da yake daidai.