Littafi Mai Tsarki

Mar 5:6-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Da dai ya hango Yesu, sai ya sheƙo a guje ya fāɗi a gabansa,

7. ya ƙwala ihu ya ce, “Ina ruwanka da ni, Yesu Ɗan Allah Maɗaukaki? Na gama ka da Allah, kada ka yi mini azaba.”

8. Ya faɗi haka ne domin Yesu ya ce masa, “Rabu da mutumin nan, kai wannan baƙin aljan!”

9. Yesu ya tambaye shi, “Me sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Tuli, don muna da yawa.”

10. Sai ya roƙi Yesu da gaske kada ya kore su daga ƙasar.

11. To, wurin nan kuwa da wani babban garken alade na kiwo a gangaren dutsen.

12. Aljannun nan suka roƙe shi suke ce, “Tura mu wajen aladun nan, mu shiga su.”

13. Ya kuwa yardar musu. Sai baƙaƙen aljannun suka fita, suka shiga aladun. Garken kuwa wajen alade dubu biyu, suka rugungunto ta gangaren, suka fāɗa tekun, suka halaka a ruwa.