Littafi Mai Tsarki

Luk 9:49-57 Littafi Mai Tsarki (HAU)

49. Sai Yahaya ya amsa ya ce, “Maigida, mun ga wani yana fitar da aljannu da sunanka, mun kuwa hana shi, domin ba ya binmu.”

50. Amma Yesu ya ce masa, “Kada ku hana shi. Ai, duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”

51. Da lokacin karɓarsa a Sama ya gabato, ya himmantu sosai ga zuwa Urushalima.

52. Sai ya aiki jakadu su riga shi gaba, suka kuwa tafi suka shiga wani ƙauyen Samariyawa su shisshirya masa.

53. Amma Samariyawa suka ƙi karɓarsa, domin niyyarsa duk a kan Urushalima take.

54. Da almajiransa Yakubu da Yahaya suka ga haka suka ce, “Ya Ubangiji, ko kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama ta lashe su?”

55. Amma ya juya, ya tsawata musu.

56. Sai suka ci gaba, suka tafi wani ƙauye.

57. Suna tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka duk inda za ka.”