Littafi Mai Tsarki

Luk 20:33-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

33. To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai ɗin sun aure ta.”

34. Sai Yesu ya ce musu, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna aurarwa.

35. Amma waɗanda aka ga sun cancanci samun shiga wancan zamani da kuma tashin nan daga matattu, ba za su yi aure ko aurarwa ba.

36. Ba shi yiwuwa su sāke mutuwa, don daidai suke da mala'iku, 'ya'yan Allah ne kuwa, da yake 'ya'yan tashin matattu ne.

37. Game da tashin matattu kuwa, ai, Musa ma ya faɗa, a labarin kurmin, inda ya kira Ubangiji, Allahn Ibrahim, da Allahn Ishaku, da Allahn Yakubu.

38. Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba. Don a wurinsa duka rayayyu ne.”

39. Sai waɗansu malaman Attaura suka amsa suka ce, “Malam, ka faɗi daidai.”

40. Daga nan kuma ba su yi ƙarfin halin tambayarsa wani abu ba.

41. Amma ya ce musu, “Ƙaƙa za su ce Almasihu ɗan Dawuda ne?

42. Domin Dawuda da kansa a Zabura ya ce,‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,“Zauna a damana,

43. Sai na sa ka take maƙiyanka.” ’