Littafi Mai Tsarki

Luk 20:17-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Amma ya dube su, ya ce, “Wannan da yake a rubuce fa cewa,‘Dutsen da magina suka ƙi,Shi ne ya zama mafificin dutsen gini?’

18. Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje, amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.”

19. Nan take malaman Attaura da manyan firistoci suka nema su kama Yesu, don sun lura a kansu ne ya ba da misalin, amma suna jin tsoron jama'a.

20. Sai suka yi ta haƙwansa, suka aiki 'yan rahoto, su kuwa suka nuna kamar su masu adalci ne, da nufin su kama shi a maganarsa, su kuma ba da shi ga mai mulki ya hukunta shi.

21. Suka tambaye shi suka ce, “Malam, ai, mun sani maganarka da koyarwarka duk gaskiya ne. Ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi.

22. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa babu?”

23. Shi kuwa ya gane makircinsu, ya ce musu,

24. “Ku nuna mini dinari. Surar wa da sunan wa yake a jikinsa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”

25. Sai ya ce musu, “To, ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.”

26. Sai suka kasa kama shi a kan wannan magana gaban mutane. Saboda kuma mamakin amsarsa, suka yi shiru.

27. Sai waɗansu Sadukiyawa suka zo wurinsa (su da suke cewa, ba tashin matattu),