Littafi Mai Tsarki

Luk 20:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Wata rana yana koyar da mutane a Haikali, yana yi musu bishara, sai ga manyan firistoci da malaman Attaura, da shugabanni suka matso,

2. suka ce masa, “Gaya mana da wane izini kake yin abubuwan nan, ko kuwa wa ya ba ka izinin?”

3. Sai ya amsa musu ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku gaya mini,

4. baftismar da Yahaya ya yi, daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce?”