Littafi Mai Tsarki

A.m. 3:20-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. ya kuma aiko da Almasihun da aka ƙaddara muku tun dā, wato Yesu,

21. wanda lalle ne ya zauna a Sama, har kafin lokacin nan na sabunta dukkan abubuwa da Allah ya faɗa tun zamanin dā ta bakin annabawansa tsarkaka.

22. Musa ma ya ce, ‘Ubangiji Allah zai tasar muku da wani annabi daga cikin 'yan'uwanku, kamar yadda ya tashe ni. Lalle ne ku saurari duk abin da ya faɗa muku.

23. Zai zamana kuma duk wanda ya ƙi sauraron annabin nan, za a hallaka shi daga cikin jama'a.’

24. Hakika dukan annabawa da suka yi annabci, wato tun daga kan Sama'ila da waɗanda suka zo daga baya, duk sun yi faɗi a kan waɗannan kwanakin.

25. Ku ne tsatson annabawa, ku ne kuma magadan alkawarin da Allah ya yi wa kakanninku, da ya ce wa Ibrahim, ‘Ta zuriyarka ne za a yi wa dukkan kabilan duniya albarka.’