Littafi Mai Tsarki

Zab 78:67-72 Littafi Mai Tsarki (HAU)

67. Ubangiji ya rabu da zuriyar Yusufu,Bai kuma zaɓi kabilar Ifraimu ba.

68. A maimakonsu sai ya zaɓi kabilar Yahuza.Ya zaɓi Dutsen Sihiyona, wanda yake ƙauna ƙwarai.

69. A can ya gina Haikalinsa,Kamar wurin zamansa a Sama.Ya kafa shi da ƙarfi kamar duniya,Tabbatacce a kowane lokaci.

70. Ya zaɓi bawansa Dawuda,Ya ɗauko shi daga wurin kiwon tumaki,

71. Ya ɗauko shi daga inda yake lura da 'yan raguna.Ya naɗa shi Sarkin Isra'ila,Ya naɗa shi makiyayin jama'ar Allah.

72. Dawuda kuwa ya lura da su da zuciya ɗaya,Da gwaninta kuma ya bi da su.