3. Daga sammai Allah zai amsa mini,Zai kori waɗanda suka tasar mini,Allah zai nuna mini madawwamiyar ƙaunarsa da amincinsa.
4. Raina yana tsakiyar zakoki,Na kwanta a tsakiyar waɗanda suka yi niyyar cinye mutane.Haƙoransu kamar māsu da kibau suke,Harsunansu masu kaifi ne kamar takobi.
5. Ka bayyana girmanka ya Allah, a sararin sama,Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!
6. Maƙiyana sun kafa tarko don su kama ni,Damuwa ta fi ƙarfina.Sun yi wushefe a kan hanyata,Amma su da kansu suka fāɗa a ciki.
7. A shirye nake, ya Allah,Na shirya sosai!Zan raira waƙoƙi in yabe ka!
8. Ka farka, ya raina!Ku farka, molona da garayata!Zan sa rana ta farka!
9. Zan gode maka a cikin sauran al'umma, ya Ubangiji!Zan yabe ka a cikin jama'a!
10. Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har sammai,Amincinka kuma har sararin sammai.
11. Ka bayyana girmanka, ya Allah, a sararin sama,Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!