Zab

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Littafi Mai Tsarki

Zab 48 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Sihiyona Mai Daraja, Birnin Allah

1. Ubangiji mai girma ne,Dole kuwa a yabe shi da girmamawa a birnin Allahnmu,A kan tsattsarkan dutsensa.

2. Dutsen Sihiyona, dutse mai tsawo,Mai kyan gani ne na Allah,Birnin babban Sarki.Yakan kawo farin ciki ga dukan duniya!

3. Allah ya nuna akwai zaman lafiya a wurinsa,A kagarar birnin.

4. Sarakuna suka tattaru,Suka zo Dutsen Sihiyona,

5. Da suka gan shi sai suka yi mamaki,Suka tsorata suka gudu.

6. Tsoro ya kama su suka razana,Kamar mace wadda take gab da haihuwa.

7. Allah yakan hallaka manyan jiragen ruwa da iskar gabas.

8. Mun ji labarin waɗannan al'amura,Yanzu kuwa mun gan suA birnin Allahnmu, Mai Runduna,Zai kiyaye birnin lafiya har abada.

9. A cikin Haikalinka, ya Allah,Muna tunanin madawwamiyar ƙaunarka.

10. A ko'ina jama'a suna yabonka,Sunanka ya game duniya duka.Kana mulki da adalci.

11. Bari jama'ar Sihiyona su yi murna!Gama kana shari'a ta gaskiya,Bari biranen Yahuza su yi farin ciki.

12. Ku tafi ku kewaye Dutsen Sihiyona,Ku ƙirga yawan hasumiyarsa.

13. Ku lura da garukanta, ku bincike kagaranta,Saboda ku iya faɗa wa tsara mai zuwa,

14. Cewa wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin,Shi ne zai bishe mu a dukan zamanai masu zuwa.