Littafi Mai Tsarki

Zab 44:22-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Ya Allah, saboda kai ne ake karkashe mu a kowane lokaci,Ake kuma maishe mu kamar tumakin da za a yanyanka.

23. Ka tashi, ya Ubangiji! Me ya sa kake zama kamar mai barci?Ka tashi! Kada ka yashe mu har abada!

24. Me ya sa ka ɓuya mana?Kada ka manta da ƙuncinmu da wahalarmu!

25. Mun fāɗi, an turmushe mu a ƙasa,An bar mu kwance cikin ƙura.