Littafi Mai Tsarki

Zab 35:23-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Ka tashi, ya Ubangiji, ka kāre ni.Ya Allah ka tashi, ka bi mini hakkina.

24. Kai mai adalci ne, ya Ubangiji, ka shaida rashin laifina,Kada ka bar maƙiyana su ƙyaface ni, ya Allahna!

25. Kada ka bar su su ce wa kansu,“Madalla! Da ma abin da muke so ke nan!”Kada ka bar su su ce,“Mun rinjaye shi!”

26. Ka sa waɗanda suka ƙyaface ni a wahalata,A rinjaye su, su ruɗe.Ka sa waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni,Su sha kunya da wulakanci!

27. Ka sa waɗanda suke murna da kuɓutataSu yi ta sowa ta murna, suna cewa,“Ubangiji mai girma ne!Yana murna da cin nasarar bawansa!”

28. Sa'an nan zan yi shelar adalcinka,Dukan yini kuwa zan yi ta yabonka.