Littafi Mai Tsarki

Mar 11:14-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Sai ya ce wa ɓauren, “Kada kowa ya ƙara cin 'ya'yanka har abada!” Almajiransa kuwa suna ji.

15. Suka iso Urushalima. Ya shiga Haikalin ya fara korar masu saye da sayarwa daga ciki, ya kuma birkice teburorin 'yan canjin kuɗi da kujerun masu sayar da tattabarai,

16. ya kuma hana kowa ratsa Haikalin ɗauke da wani abu.

17. Sai ya yi musu gargaɗi ya ce, “Ashe, ba a rubuce yake ba cewa, ‘Za a kira masujadata ɗakin addu'a na dukkan al'ummai’? Amma ku kun maishe shi kogon 'yan fashi.”

18. Da manyan firistoci da malaman Attaura suka ji wannan magana suka kuma nemi hanyar hallaka shi, saboda sun tsorata da shi, don duk jama'a na mamaki da koyarwa tasa.

19. Kowace yamma kuwa Yesu yakan fita gari.

20. Suna wucewa da safe, sai suka ga ɓauren nan ya bushe har saiwarsa.

21. Bitrus kuwa ya tuna, sai ya ce masa, “Ya Shugaba, dubi! Ɓauren nan da ka la'anta ya bushe!”

22. Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku gaskata da Allah.