Littafi Mai Tsarki

Luk 11:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Wata rana Yesu yana addu'a a wani wuri. Bayan da ya gama, sai wani a cikin almajiransa ya ce masa, “Ya Ubangiji, ka koya mana addu'a, kamar yadda Yahaya ya koya wa almajiransa.”

2. Sai ya ce musu, “In kuna addu'a ku ce,‘Ya Uba, a kiyaye sunanka da tsarki,Mulkinka yă zo,

3. Ka ba mu abincin yau da na kullum.

4. Ka gafarta mana zunubanmu, gama mu ma muna gafarta wa duk wanda yake yi mana laifi.Kada ka kai mu wurin jaraba.’ ”

5. Ya kuma gaya musu, “Misali, idan waninku yana da amini, ya je wurinsa da tsakar dare ya ce masa, ‘Wāne, ranta mini gurasa uku mana,