Littafi Mai Tsarki

Luk 1:64-67 Littafi Mai Tsarki (HAU)

64. Nan da nan ya sami baki, kwaɗon harshensa ya saku, ya fara magana, yana yabon Allah.

65. Sai tsoro ya kama dukan maƙwabtansu. Aka yi ta baza labarin duk waɗannan al'amura ko'ina a dukan ƙasa mai duwatsu ta Yahudiya.

66. Duk waɗanda suka ji kuwa suka riƙe a zuciyarsu, suna cewa, “Me ke nan ɗan yaron nan zai zama?” Gama ikon Ubangiji yana tare da shi.

67. Sai aka cika ubansa Zakariya da Ruhu Mai Tsarki, ya yi annabci, ya ce,