Littafi Mai Tsarki

Luk 1:43-55 Littafi Mai Tsarki (HAU)

43. Ta yaya wannan alheri ya same ni, har da uwar Ubangijina za ta zo gare ni?

44. Domin kuwa da jin muryarki ta gaisuwa a kunnena, sai jaririn ya motsa da ƙarfi a cikina domin farin ciki.

45. Albarka tā tabbata ga wadda ta gaskata, domin za a cika abubuwan da Ubangiji ya aiko a faɗa mata.”

46. Sai Maryamu ta ce,“Zuciyata na ɗaukaka shi, Ubangiji,

47. Allah Mai Cetona, da shi ruhuna yake ta farin ciki,

48. Domin fa shi ya dubi ƙasƙancin baiwa tasa.Ga shi, jama'a ta dukan zamanai,Za su ce mini mai albarka ce nan gaba.

49. Domin fa shi da yake Mai Iko,Manyan al'amura ya yi mini,Sunansa labudda mai tsarki ne.

50. Daga zamanai ya zuwa wani zamani,Jinƙansa yana ga waɗanda suke tsoronsa.

51. Manyan ayyuka da ya yi,Masu girmankai, su da dabarbarunsu ya warwatsa.

52. Ya firfitar da sarakuna a sarauta,Ya ɗaukaka ƙasƙantattu.

53. Mayunwata ya ƙosar da abubuwan alheri,Mawadata kuwa ya sallame su hannu wofi.

54. Ya taimaka wa baransa Isra'ila,Domin yana tunawa da jinƙansa.

55. Ya cika faɗarsa ga kakanninmu,Ga Ibrahim da zuriyarsa, har abada.”