Littafi Mai Tsarki

L. Mah 8:27-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Gidiyon kuwa ya yi gunki da zinariyar, ya ajiye a birninsa, wato Ofra. Isra'ilawa kuma suka bar bin Allah, suka tafi can domin su yi wa gunkin sujada, ya zama tarko ga Gidiyon da iyalinsa.

28. Da haka Isra'ilawa suka mallaki Madayanawa har ba su zamar musu barazana ba. Ƙasar kuwa ta zauna lafiya shekara arba'in a zamanin Gidiyon.

29. Gidiyon kuwa ya tafi ya zauna a gidansa na kansa.

30. Yana kuma da 'ya'ya maza saba'in, gama yana da mata da yawa.

31. Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take a Shekem, ta haifi masa ɗa, ya sa masa suna Abimelek.

32. Sa'an nan Gidiyon, ɗan Yowash, ya rasu da kyakkyawan tsufa. Aka binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa, a Ofra, birnin kabilar Abiyezer.