Littafi Mai Tsarki

L. Mah 5:22-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Sa'an nan dawakai sun yi ta rishiSuna ƙwaƙular ƙasa da kofatansu.

23. Mala'ikan Ubangiji ya ce,“Ka la'anta Meroz,Ka la'anta mazauna cikinta sosai,Gama ba su kawo wa Ubangiji gudunmawa ba,Su zo su yi yaƙi kamar sojoji dominsa.”

24. Wadda ta fi kowa sa'a daga cikin mata, sai Yayel,Matar Eber, Bakene,Wadda ta fi kowa sa'a daga cikin matan da suke a alfarwai.