Littafi Mai Tsarki

L. Mah 5:13-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Sa'an nan amintattu sun zo wurin shugabanninsu,Jama'ar Ubangiji suka zo wurina a shirye domin yaƙi.

14. Daga Ifrraimu mutane suka gangaro zuwa kwari,Bayan kabilar Biliyaminu da mutanenta.Daga Makir shugabannin sojoji suka zo,Daga Zabaluna kuma jarumawa suka gangaro.

15. Shugabannin Issaka suna tare da Debora,Hakika, Issaka ya zo, Barak kuma ya zo,Suka bi bayansu zuwa kwari.Amma kabilar Ra'ubainu ta rarrabu,Ba su shawarta su zo ba.

16. Don me suka tsaya daga baya tare da tumaki?Don su saurari makiyaya na kiran garkuna?Hakika kabilar Ra'ubainu ta rarrabu,Ba su shawarta su zo ba.

17. Kabilar Gad suna tsaya a gabashin Urdun,Kabilar Dan kuma ta tsaya a wuraren kiwo.Kabilar Ashiru ta zauna a bakin teku,Sun zauna a gefen teku.

18. Amma mutanen Zabaluna da na NaftaliSuka kasai da ransu a bakin dāga.

19. Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi a Ta'anak,A rafin Magiddo.Sarakunan Kan'ana suka yi yaƙi,Amma ba su kwashe azurfa ba.

20. Daga sama, taurari suka yi yaƙi,Suna gilmawa a sararin samaSuka yi yaƙi da Sisera.