Littafi Mai Tsarki

K. Mag 30:3-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Ban koyi hikima ba,Ban kuwa san kome game da Allah ba.

4. Wa ya taɓa hawa cikin Sama ya sauko?Wa ya taɓa kama iska cikin tafin hannunsa?Wa ya taɓa ƙunshe ruwa cikin rigarsa?Wa kuma ya kafa iyakar duniya?Ina sunansa, ina kuma sunan ɗansa?Hakika ka sani!

5. “Kowace maganar Allah takan tabbata. Shi garkuwa ne ga waɗanda suke fakewa a wurinsa.

6. Kada ka yi ƙari a kan maganarsa, don kada ya tsauta maka, a kuma bayyana kai maƙaryaci ne.”

7. Abu biyu na roƙe ka, kada ka hana mini su kafin in mutu.

8. Ka kawar da ƙarya nesa da ni. Kada ka ba ni talauci ko dukiya, sai dai ka ba ni abinci daidai da bukatata,

9. don kada in wadata, har in yi musunka, in ce, “Wane ne Ubangiji?” Kada kuwa in yi talauci har in yi sata in saɓi sunan Allahna.

10. Kada ka kushe bara a wurin maigidansa domin kada ka yi laifin da zai sa a la'ance ka.

11. Akwai waɗansu mutane da sukan zagi iyayensu maza, ba sukan kuma nuna godiya ga iyayensu mata ba.

12. Akwai waɗansu mutanen da suke ganin kansu tsarkaka ne, alhali kuwa ƙazamai ne su.

13. Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama'a ƙallon raini suna ɗaurin gira.

14. Akwai waɗansu mutane waɗanda haƙoransu takuba ne, mataunansu kuma wuƙaƙe ne, don su cinye matalauta da masu fatara daga duniya.