Littafi Mai Tsarki

K. Mag 14:8-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Me ya sa haziƙi yake da hikima? Domin ya san abin da zai yi. Me ya sa dakiki yake wauta? Domin yana ganin kansa masani ne.

9. Idan wawaye sun yi zunubi ba sukan kula ba, amma mutanen kirki sukan nemi gafara.

10. Ɓacin ranka naka ne, murnarka kuwa ba za ka raba da wani ba.

11. Gidan mutumin kirki ba zai rushe ba bayan da an lalatar da gidan mugun mutum.

12. Hanyar da kake tsammani ita ce daidai, za ta kai ka ga hallaka.

13. Dariyar mutum takan ɓoye baƙin cikinsa. Sa'ad da murna ta tafi, ko yaushe baƙin ciki yana nan.

14. Mugu zai sami abin da ya cancance shi, mutumin kirki kuma zai sami sakayyar ayyukansa.

15. Wawa yakan gaskata kowane abu, amma mai la'akari yana lura da takawarsa.