Littafi Mai Tsarki

K. Mag 1:13-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Za mu sami dukiya iri iri, mu cika gidajenmu da ganima!

14. Ka zo ka haɗa kai da mu, dukanmu kuwa za mu raba abin da muka sato.”

15. Ɗana, kada ka gama kanka da irin waɗannan mutane, ka yi nesa da su.

16. Ba su kasalar aikata mugunta, kullum a shirye suke su yi kisankai.

17. Ba shi da amfani a kafa tarko a idon tsuntsun da ake so a kama.

18. Amma waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko. Ba za su kama kome ba, sai rayukansu.