Littafi Mai Tsarki

Fit 21:17-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. “Wanda ya raina mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lalle kashe shi za a yi.

18. “Idan mutane suka yi faɗa, ɗayan ya jefa ɗayan da dutse, ko ya naushe shi amma bai mutu ba, sai dai ya yi ta jiyya,

19. idan mutumin ya sāke tashi ya yi tafiya ko da yana dogarawa da sanda, wanda ya buge shi zai kuɓuta, sai dai zai biya diyyar lokacin da ya ɓāta masa, ya kuma lura da shi har ya warke sarai.