Littafi Mai Tsarki

A.m. 13:37-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

37. Amma shi wannan da Allah ya tashe shi, bai ruɓa ba.

38. Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku sani albarkacin mutumin nan ne ake sanar da ku gafarar zunubanku.

39. Ta gare shi kuma, duk masu ba da gaskiya suka kuɓuta daga dukan abubuwan da ba dama Shari'ar Musa ta kuɓutar da ku.

40. Saboda haka sai ku mai da hankali, kada abin nan da littattafan annabawa suke faɗa ya aukar muku, wato

41. ‘Ga shi, ku masu rainako,Za ku ruɗe don mamaki, ku shuɗe!Domin zan yi wani aiki a zamaninku,Aikin da ba yadda za a yi ku gaskata,Ko da wani ya gaya muku.’ ”

42. Suna fita majami'a ke nan, sai mutane suka roƙe su su ƙara yi musu wannan magana a ran Asabar mai zuwa.

43. Da jama'a suka watse, Yahudawa da yawa, da kuma waɗanda suka shiga Yahudanci, masu ibada, suka bi Bulus da Barnaba. Su kuma suka yi musu magana, suna yi musu gargaɗi su zauna a cikin alherin Allah.

44. Da Asabar ta kewayo, kusan duk birnin, suka hallara su ji Maganar Allah.

45. Amma da Yahudawa suka ga taro masu yawa, suka yi kishi gaya, suka yi ta musun abubuwan da Bulus ya faɗa, suna zaginsa.