Littafi Mai Tsarki

Afi 5:28-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Ta haka ya wajaba maza su ƙaunaci matansu, jikinsu ke nan suke yi wa. Ai, wanda ya ƙaunaci matarsa, ya ƙaunaci kansa ke nan.

29. Domin ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai ya rene shi, ya yi tattalinsa, kamar yadda Almasihu yake yi wa Ikkilisiya,

30. domin mu gaɓoɓin jikinsa ne.

31. “Saboda haka ne, mutum sai ya bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, ya manne wa matarsa, su biyu su zama jiki guda.”

32. Wannan asiri muhimmi ne, ni kuwa ina nufin Almasihu ne da ikkilisiya.