Littafi Mai Tsarki

Zab 94:16-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Wa zai tsaya mini gāba da mugaye?Wa zai goyi bayana gāba da masu aikata mugunta?

17. Da ba domin Ubangiji ya taimake ni ba,Ai, da tuni na kai ƙasar da ba a motsi.

18. Na ce, “Ina kan fāɗuwa,”Amma, ya Ubangiji, madawwamiyar ƙaunarka ta riƙe ni.

19. Sa'ad da nake alhini, ina cikin damuwa,Ka ta'azantar da ni, ka sa in yi murna.

20. Ba ruwanka da alƙalai azzalumai, marasa gaskiya,Waɗanda suka mai da rashin gaskiya ita ce gaskiyarsu,

21. Sukan shirya wa mutanen kirki maƙarƙashiya,Sukan yanke wa marar laifi hukuncin kisa.