Littafi Mai Tsarki

Zab 86:4-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Ka sa bawanka yă yi murna, ya Ubangiji,Saboda addu'o'ina sun hau zuwa gare ka.

5. Ya Ubangiji, kai managarci ne, mai yin gafara,Cike kake da madawwamiyar ƙauna ga dukan waɗanda suke yin addu'a gare ka.

6. Ka ji addu'ata, ya Ubangiji,Ka ji kukana na neman taimako!

7. Nakan kira gare ka a lokacin wahala,Saboda kakan amsa addu'ata.

8. Ba wani allah kamarka, ya Ubangiji,Ba ko ɗaya, ba wanda zai iya aikata abin da kake aikatawa.

9. Dukan sauran al'umma da ka halittaZa su zo su rusuna har ƙasa a gabanka.Za su yabi girmanka,