12. Kada ka yi nisa da ni haka, ya Allah,Ka yi hanzari ka taimake ni, ya Allahna!
13. Ka sa a kori waɗanda suka tasar mini,A hallaka su!Ka sa a kunyata waɗanda suke ƙoƙari su cuce ni,A wulakanta su sarai!
14. A koyaushe zan sa zuciya gare ka,Zan yi ta yabonka.
15. Zan ba da labarin adalcinka,Zan yi magana a kan cetonka duk yini,Ko da yake ya fi ƙarfin in san shi duka.