Littafi Mai Tsarki

Zab 69:32-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Sa'ad da masu bukata suka ga wannan za su yi murna,Waɗanda suke yi wa Allah sujada kuwa za a ƙarfafa su.

33. Ubangiji yana kasa kunne ga masu bukata,Bai manta da jama'arsa da suke a kurkuku ba.

34. Ku yabi Allah, ku al'arshi da duniya, ku yabi Allah,Tekuna da dukan talikan da suke cikinsu!

35. Gama zai ceci Sihiyona,Ya sāke gina garuruwan Yahuza,Jama'arsa za su zauna a wurin, su mallaki ƙasar.

36. Zuriyar bayinsa za su gāje ta,Masu ƙaunarsa za su zauna a wurin.