31. Wannan zai daɗaɗa wa Ubangiji raiFiye da hadayar bijimi,Fiye da a ba shi bijimi bana bakwai.
32. Sa'ad da masu bukata suka ga wannan za su yi murna,Waɗanda suke yi wa Allah sujada kuwa za a ƙarfafa su.
33. Ubangiji yana kasa kunne ga masu bukata,Bai manta da jama'arsa da suke a kurkuku ba.
34. Ku yabi Allah, ku al'arshi da duniya, ku yabi Allah,Tekuna da dukan talikan da suke cikinsu!