Littafi Mai Tsarki

Zab 68:17-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Daga Sinai da dubban manyan karusansa,Ubangiji ya zo tsattsarkan Haikalinsa.

18. Ya hau kan tsaunukaTare da ɗumbun waɗanda ya kamo daga yaƙi,Yana karɓar kyautai daga wurin mutane,Daga wurin 'yan tawaye kuma.Ubangiji Allah zai zauna a can.

19. Ku yabi Ubangiji,Wanda yake ɗaukar nawayarmu ta yau da kullum,Shi ne Allah wanda ya cece mu.

20. Allahnmu, Allah Mai Ceto ne,Shi ne Ubangiji, Ubangijinmu,Wanda yake cetonmu daga mutuwa.

21. Hakika Allah zai farfashe kawunan abokan gābansa,Da na waɗanda suka nace bin hanyoyinsu na zunubi.

22. Ubangiji ya ce, “Zan komo da su daga Bashan,Zan komo da su daga zurfin teku,

23. Don ku wanke sawayenku a cikin jinin maƙiyanku,Karnukanku kuwa za su lashe iyakar abin da suke so.”

24. Ya Allah, jama'a duka sun ga irin tafiyarka ta nasara,Irin tafiyar Allah, Sarkina, zuwa tsattsarkan wurinsa.