Littafi Mai Tsarki

Zab 66:8-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ku yabi Allahnmu, ya ku dukan al'ummai,Bari a ji yabon da kuke yi masa.

9. Shi ne yake rayar da mu,Bai kuwa yarda mu fāɗi ba.

10. Ka jarraba mu, ya Allah,Kamar yadda ake tace azurfa da wuta,Haka nan ka jarraba mu.

11. Ka bar mu muka fāɗa a tarko,Ka ɗora mana kaya masu nauyi.

12. Ka bar maƙiyanmu suka tattaka mu,Mun ratsa ta cikin wuta da rigyawa,Amma yanzu ka kawo mu a lafiyayyen wuri.

13. Zan kawo hadayun ƙonawa a ɗakinka,Zan miƙa maka abin da na alkawarta.

14. Zan ba ka abin da na ce zan bayar,A lokacin da nake shan wahala.

15. Zan miƙa tumaki don a ƙona a kan bagade,Nan za a ji ƙanshi mai daɗi na ƙonannun awaki,Zan miƙa hadayu na bijimai da na awaki.

16. Ku zo ku ji, dukanku, ku da kuke girmama Allah,Ni kuwa zan faɗa muku abin da ya yi mini.