Littafi Mai Tsarki

Zab 49:5-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Don me zan ji tsoro a lokacin hatsari,Sa'ad da mugaye suka kewaye ni,

6. Mutanen da suke dogara ga dukiyarsu,Waɗanda suke fariya saboda yawan wadatarsu?

7. Har abada mutum ba zai iya fansar wani ba,Ba kuwa zai iya biyan kuɗin ransa ga Allah ba.

8. Gama kuɗin biyan ran mutum ba shi da iyaka.Abin da zai iya biya, sam ba zai isa ba,

9. Ba kuwa zai rayar da shi,Ko ya hana shi mutuwa har abada ba.

10. Yakan sa masu hikima su ma su mutu,Haka nan ma wawaye da mutanen banza,Za su mutu su bar dukiyarsu ga zuriyarsu.

11. Kaburburansu za su zama gidajensu har abada,Can za su kasance kullum,Ko da yake a dā suna da ƙasa ta kansu.

12. Girman mutum ba zai hana shi mutuwa ba,Zai mutu kamar dabba.

13. Dubi abin da zai faru ga waɗanda suke dogara ga kansu,Da irin ƙaddarar waɗanda dukiya ta ishe su.

14. Za a ƙaddara su ga mutuwa kamar tumaki,Mutuwa ce za ta yi kiwonsu.Da safe adalai za su ci nasara a kansu,Sa'ad da gawawwakinsu suke ruɓewa a ƙasar matattu,Nesa da gidajensu.

15. Amma Allah zai fanshe ni,Zai ɗauke ni daga ikon mutuwa.

16. Kada ka damu sa'ad da mutum ya zama attajiri,Ko kuwa dukiyarsa ta ƙasaita,