Littafi Mai Tsarki

Zab 39:11-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Kakan hukunta zunuban mutum ta wurin tsautawarka,Kamar yadda asu yake lalata abu.Hakika mutum bai fi shaƙar iska ba!

12. “Ka ji addu'ata, ya Ubangiji,Ka kuma kasa kunne ga roƙona,Kada ka yi shiru sa'ad da na yi kuka gare ka!Yadda dukan kakannina suka yi,Ni baƙonka ne na ɗan lokaci.

13. Ka ƙyale ni ko zan sami kwanciyar rai,Kafin in tafi, ai, tawa ta ƙāre.”