Littafi Mai Tsarki

Zab 37:31-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.

32. Mugu yakan yi fakon mutumin kirki,Yă yi ƙoƙari yă kashe shi,

33. Amma Ubangiji ba zai bar shi a hannun magabtansa ba,Ko kuwa yă bari a kāshe shiSa'ad da ake masa shari'a.

34. Ka sa zuciyarka ga UbangijiKa kiyaye dokokinsa,Shi zai ba ka ƙarfin da za ka mallaki ƙasar,Za ka kuwa ga an kori mugaye.

35. Na ga wani mugu, azzalumi,Ya fi kowa tsayi,Kamar itacen al'ul na Lebanon,