Littafi Mai Tsarki

Zab 29:8-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Muryarsa ta sa hamada ta girgiza,Ta girgiza hamadar Kadesh.

9. Muryar Ubangiji ta sa barewa ta haihu,Ta sa itatuwa su kakkaɓe,Sa'ad da aka yi sowa a cikin Haikalinsa,Aka ce, “Daukaka ga Allah!”

10. Ubangiji yana sarautar ruwa mai zurfi,Yana sarauta kamar sarki har abada.

11. Ubangiji yana ba jama'arsa ƙarfi,Ya sa musu albarka da salama.