Littafi Mai Tsarki

Zab 22:27-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Dukan al'ummai za su tuna da Ubangiji,Za su zo gare shi daga ko'ina a duniya,Dukan kabilai za su yi masa sujada.

28. Ubangiji Sarki ne,Yana mulki a kan al'ummai.

29. Masu girmankai duka za su rusuna masa,'Yan adam duka za su rusuna masa,Dukan waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa.

30. Zuriya masu zuwa za su bauta masa,Mutane za su ambaci Ubangiji ga zuriya mai zuwa.

31. Mutanen da ba a haifa ba tukuna, za a faɗa musu,“Ubangiji ya ceci jama'arsa!”