8. A Masar ne ya karkashe 'ya'yan fari na mutane da na dabbobi.
9. A can ne ya aikata mu'ujizai da al'ajabai,Domin ya hukunta Fir'auna da dukan hukumar ƙasarsa.
10. Ya hallakar da sauran al'umma masu yawa,Ya karkashe sarakuna masu iko, wato
11. Sihon, Sarkin Amoriyawa, da Og, Sarkin Bashan,Da dukan sarakunan Kan'ana.
12. Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa,Ya ba da ita ga Isra'ila.
13. Ya Ubangiji, kullayaumi mutane za su sani kai ne Allah,Dukan tsararraki za su tuna da kai.