Littafi Mai Tsarki

Zab 105:24-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Ubangiji ya sa jama'arsa suka hayayyafa da yawa,Ya sa su fi ƙarfin maƙiyansu.

25. Ya sa Masarawa suka ƙi jinin jama'arsa,Suka yi wa bayinsa munafunci.

26. Sai ya aiki bayinsa Musa da Haruna, waɗanda ya zaɓa.

27. Suka aikata manya manyan ayyuka na Allah,Suka kuma yi ayyukan al'ajabi a Masar.

28. Ya aika da duhu a bisa ƙasar.Musa da Haruna ba su tayar wa umarnansa ba.

29. Ya mai da ruwan kogunansu su zama jini,Ya karkashe kifayensu duka.

30. Ƙasarsu ta cika da kwaɗi,Har a fādar sarki.

31. Allah ya ba da umarni, sai ƙudaje da ƙwariSuka cika dukan ƙasar.

32. Ya aiki ƙanƙara da tsawa a bisa ƙasarsuMaimakon ruwan sama.

33. Ya lalatar da 'ya'yan inabinsu da itatuwan ɓaurensu,Ya kakkarya itatuwansu.

34. Ya ba da umarni, sai fāri suka zo,Dubun dubbai da ba su ƙidayuwa.

35. Suka cinye dukan tsire-tsire na ƙasa.Suka cinye dukan amfanin gonaki.

36. Ya karkashe dukan 'ya'yan fari mazaNa dukan iyalan Masarawa.

37. Sa'an nan ya bi da Isra'ilawa, suka fita,Suka kwashi azurfa da zinariya,Dukansu kuma ƙarfafa ne lafiyayyu.

38. Masarawa suka yi murna da fitarsu,Gama sun tsoratar da su.