20. Sa'an nan Sarkin Masar ya sake shi,Mai mulkin dukan sauran al'umma ya 'yantar da shi.
21. Ya sa shi ya lura da mulkinsa,Ya sa shi ya yi mulki a bisa dukan ƙasar.
22. Ya ba shi cikakken iko bisa dukan ma'aikatan hukuma.Ya ba shi ikon umartar mashawartansa.
23. Sa'an nan Yakubu ya tafi Masar,Ya zauna a ƙasar.
24. Ubangiji ya sa jama'arsa suka hayayyafa da yawa,Ya sa su fi ƙarfin maƙiyansu.