Littafi Mai Tsarki

Zab 105:16-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Sa'ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu,Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare,

17. Sai ya aika da Yusufu ya riga su zuwa,Shi wanda aka sayar da shi kamar bawa.

18. Ƙafafunsa suka yi rauni saboda an ɗaure su da sarƙa,Aka kuma sa wa wuyansa ƙuƙumi na baƙin ƙarfe,

19. Har kafin faɗar da ya yi, ta cika.Maganar Ubangiji ta tabbatar da gaskiyar abin da ya faɗa.

20. Sa'an nan Sarkin Masar ya sake shi,Mai mulkin dukan sauran al'umma ya 'yantar da shi.

21. Ya sa shi ya lura da mulkinsa,Ya sa shi ya yi mulki a bisa dukan ƙasar.