Littafi Mai Tsarki

Zab 105:12-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Jama'ar Ubangiji kima ne,Baƙi ne kuwa a ƙasar.

13. Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa,Daga wannan mulki zuwa wancan,

14. Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba,Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.

15. Ya ce, “Kada ku taɓi bayina, zaɓaɓɓu,Kada ku cuci annabawana!”

16. Sa'ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu,Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare,

17. Sai ya aika da Yusufu ya riga su zuwa,Shi wanda aka sayar da shi kamar bawa.