Littafi Mai Tsarki

Zab 104:1-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ka yabi Ubangiji, ya raina!Ya Ubangiji Allahna, mai girma ne kai!Kana saye da ɗaukaka da daraja,

2. Ka yi lulluɓi da haske.Ka shimfiɗa sammai kamar alfarwa.

3. Ka gina wurin zamanka a bisa kan ruwan da yake sama.Gajimare ne karusanka,A bisa kan fikafikan iska kake tafiya.

4. Iska ce jakadanka,Walƙiya kuwa ita ce baiwarka.

5. Ka sa duniya ta kahu sosai a bisa harsashin gininta,Ba kuwa za a iya kawar da ita ba har abada.

6. Ka sa teku a bisanta kamar alkyabba,Ruwan kuwa ya rufe manyan duwatsu.

7. Amma sa'ad da ka tsauta wa ruwa,Sai ya tsere,Sa'ad da ya ji ka daka tsawa,Sai ya sheƙa a guje.

8. Ya haura kan duwatsu, ya gangara cikin kwaruruka,Wurin da ka shirya masa.

9. Ka ƙayyade masa kan iyaka da ba zai taɓa ƙetarewa ba,Don kada ya sāke rufe duniya.

10. Ka sa maɓuɓɓugai suka gudano cikin kwaruruka,Ka sa ruwa yana gudu tsakanin tuddai.

11. Su ne suke shayar da namomin jeji,Jakunan jeji kuma, a nan sukan kashe ƙishinsu.

12. A itatuwan da suke kusa da wurin,Tsuntsaye suke yin sheƙunansu suna ta raira waƙa.

13. Daga sararin sama kakan aiko da ruwa bisa duwatsu,Ƙasa kuwa takan cika da albarkunka.

14. Kakan sa ciyawa ta yi girma don shanu,Tsire-tsire kuma don amfanin mutum,Saboda haka mutum zai iya shuka amfanin gona,