Littafi Mai Tsarki

Zab 102:4-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. An tattake ni kamar busasshiyar ciyarwa,Ba ni da marmarin cin abinci.

5. Ina nishi da ƙarfi,Ba abin da ya ragu gare ni,In banda ƙashi da fata.

6. Ni kamar tsuntsu nake cikin hamada,Kamar mujiya a kufai.

7. Kwana nake ba barci,Na zama kamar tsuntsun da yake fama da kewaA bisa kan ɗaki.

8. Maƙiyana suna cin mutuncina dukan yini.Waɗanda suke mini ba'a,Suna la'antarwa da sunana.

9. Toka ce abincina,Hawayena kuwa sun gauraya da abin shana,

10. Sabili da fushinka da hasalarka.Ka ɗauke ni, ka jefar da ni.

11. Raina kamar inuwar maraice yake,Kamar busasshiyar ciyawa nake.

12. Amma kai, ya Ubangiji, sarki ne kai har abada,Dukan zamanai masu zuwa za su tuna da kai.

13. Za ka tashi ka ji tausayin Sihiyona,Lokaci ya yi da za ka yi mata jinƙai,Wannan shi ne lokacin!

14. Bayinka suna ƙaunarta,Ko da yake an hallakar da ita,Suna jin tausayinta,Ko da yake ta zama kufai.

15. Sauran al'umma za su ji tsoron Ubangiji,Dukan sarakunan duniya za su ji tsoron ikonsa.